Hakika Zakkah tana da mutukar muhimmanci domin duk wanda yake fitar da Zakkah kamar yadda Allah ya umarta toh tabbas dukiyar sa Allah zai tsare ta daga masifu irin su: Gobara,asari da kuma mummunar karayar arziki.
Haka kuma Zakkah tana sa mutune su dinga ganin darajar wanda ya bada ita haka Zakkah tana kawo masalaha tsakanin mai shi da maras shi. Sannan Kuma yadda ake fitar da ita shi ne ka fitar da kashi daya bisa arba'in na dukiyar ka ma'ana zaka kasa dukiyar ka gida arba'in sai ka bada guda daya kachal.
Mu gane zakkah hakkin Allah Kuma wajibi dole ne ka fitar da ita indai kana so kaga dai-dai a cikin dukiyar ka.