Friday, May 5, 2023

NASIHA

 Karka damu da idda Allah ya ajeka a rayuwa ka yadda da abun da Allah ya raba ya baka, kowanne mutum da kaddarar da Allah ya nufa agareshi ka yi amfani da iya abun ka suma ka yi rayuwarka cikin kwanciyar hankali.

Idan ka dorawa kanka sai abunda wane yayi zaka yi lalle ka hada kanka da wahala.Wasu su na bam mamaki wai sai rigar da wane  ya sa irinta lalle zasu sa, shin in tambayeka dan uwa Samunka da nasa daya ne ? ka yiwa kanka karatun ta nutsu ka zamo mai godiyar Allah a duk inda ka tsinci kanka.

 Ni Umar Usaini Kawon Kudu, Alhamdulillah na gode wa Allah, Allah ka kara Mana lafiya da wadatuwar arziki saboda Rasulillah Sallallahu alaihi wasallam, Amin ya Allah,🤲🤲🤲.



No comments:

Post a Comment

INA MUKA DOSA MATASA

 Na dade Ina tuntuntuni akan rayuwar wasu daga cikin matasa idan na tsaya nai tsumm sai na tambayi kaina amma amsar bata zoba wait shin: mat...